Alternative Espaces Citoyens Niger

Articles les plus récents


Articles les plus récents


Hira da Mallam Ali Nuhu

vendredi 23 décembre 2005
A ranar asabar 22 ga watan janairun da ya gabata ne gidan Radion Tambara tare da hadin guiwar wasu matasa yan kasa da ke nan birnin Yamai, suka gayyato yan wasan kungiyoyin dake shirya fina-finan hausa na tarayar Najeriya suka gabatar da wata gagarumar wasa da ta kayatar da yan kallonta a babban dakin wasannin motsa jiki na Palais des sports dake nan birnin yamai, da kuma a gidan kallon Cinéma Zabarkan. Daga cikin yan wasan da aka gayyato sun hada ne da Ali Nuhu, Sani Danja, Aina Ade, da dai sauransu...wannan ya baiwa jaridar Ra’ayi damar tattaunawa da shahararren jarumin nan kuma Director mai shirya fina-finan hausa da tauraruwarsa ke cigaba da haskawa ta wannan fage, wato Ali Nuhu. Da farko dai jaridar Ra’ayi ta soma tambayar sa ne da cewa : > suite


Idan gwamnati ta yaye wasan kokowar gargajiya to wane zata shayar ?

jeudi 22 décembre 2005
A fagen wasannin motsa jiki, kasar Nijar tayi fice matuka dangane da nuna kwarewa ta fannin kokowar gargajiya, inda a koda yaushe a kace za’a gudanar da wata kwambala, to lalle yan Nijar a shirye suke domin kare martabar kasar su. > suite


Ranar yaki da cutar zazzabin cizon sabro ta Afrika

jeudi 22 décembre 2005
Ranar 25 ga watan Afrilun kowace shekara rana ce da hukumar lafiya ta duniya ta kebe domin ta zama ranar yaki da cutar zazzabin cizon sabro a afrika. Ko a bana kamar dai sauran shekaru an gudanar da shagulgullan zagayowar wannan rana a sassa da dama na Afrika cikin su kuwa har da kasar Nijar. (...) > suite


Ciwon tsagiya

Babbar yekuwa ta kawar da cututtukan fitsarin jini ko ciwon tsagiya da kuma tsutsar ciki a cikin jahohin Maradi da Tawa
jeudi 22 décembre 2005
A game da namjin kokarin da hukumomi a ma’aikatar kiwon lafiya ta kasarnan ke yi domin kawar da ciwon tsagiya ko fitsarin jini da kuma cutar tsusar ciki a Nijar, wannan yasa aka kirkiro da wani bangare a ma’aikatar ta kiwon lafiya mai yaki da irin wadannan cututtuka a wannan kasa Nijar. Wannan dangare dai an kirkiro shi ne a cikin watan Maris na shekara ta 2004, inda kuma yake cigaba da gudanar da ayyukan sa na warakar da jama’a a sassa da dama na kasarnan > suite


Kiwon lafiyar yara a yanjin Maradi

jeudi 22 décembre 2005
A kowace shekara, kimanin yara yan kasa da shekaru biyar a duniya dubu goma sha daya ne dake fama da cutar tamowa, ke samun kulawar wata kungiya mai zaman kanta a yankin Maradi. > suite


lHukumar kare yancin dan adam ta kasa CNDHLF ta nemi gwamnati da ta soke tare da kwace kaddarorin da kungiyar Timidria ta mallaka

jeudi 22 décembre 2005
Shugaban kungiyar nan mai yaki bautar da jama’a a kasar Nijar mai suna Timidria Ilguelas Weila na ci gaba da kasancewa a gidan kurkukun birnin Yamai , bayan da jami’an tsaro suka yi awon gaba da shi tun ranar 28 ga watan Maris da ya gabata. Ilguelas Weila wanda aka cabke tare da wadansu manyan jami’ai na kungiyarsa , sun ci gaba da kasancewa a hannun jami’an tsaron ne har na tsawon mako daya, kafin daga bisani a saki wasu daga cikinsu kana aka ci gaba da tsare shugaban kungiyar na kasa baki daya da kuma mataimakin magatakarda na kungiyar mai kula da shiyar Tillaberi mai suna Alasan Biga. > suite


Al’amarin tsaro a mayan biranen jamhuriyar Nijar

sai cigaba da tabarbarewa yake
jeudi 22 décembre 2005
Aya ta 11 da ke kumshe a cikin Kundin tsarin mulkin kasar Nijar, ta yi furuci a game da tsaron rayuwa, lafiya da kuma dukiyoyin yan kasa. > suite


Kisan Jinjirai a Nijar

jeudi 22 décembre 2005
Kisa a wannan zamani wani abu ne mai sauki, da ya zama ruwan dare gama duniya. kisan gilla wata kalma ce da bahaushe ke anfani da ita domin bayyana cewa an fitar da rayuwar wani ko wata da gangan ba tare da aikata wani laifi ba, abin dake cigaba da faruwa a kowace safiya ta Allah a cikin (...) > suite


Ranar yancin aikin jarida ta duniya

a kasar Nijar ma an gudanar da shagulgula daban daban domin murnar zagayowar wannan rana
jeudi 22 décembre 2005
Ranar 3 ga kowane watan Mayu na shekarar meladiyya ; ta kasance ranar yanci da walwala ga aikin jarida na duniya baki daya kamar yadda majalisar dinkin duniya ta yi ammana tun cikin shekara ta 1990 ;yau shekaru goma sha biyar(15) kenan da su ka gabata. Kamar ko wace shekara ; tun soma raya wannan rana ta yan jarida a bana ma gungun kungiyoyin yan jaridu na kasar Nijar tare da hadin gyuwar da tallafin ofishin jakadancin kasar Amurka na birnin yamai ;sun gudanar da dimbin shagulgulla albarkacin wannan rana. An fara bikin ne da wasar kwallon kafa a hilin kwallon kafa na janar Seini Kountche dake nan birnin yamai. Wasar kwallon ta hada kungiyar yan jarida da ta jami’an tsaro na yan sanda ; inda kuma jami’an tsaron suka yi nasara bisa kan yan jarida da ci daya da babu .Ita dai wannan wasa ta bada shawa kwarai da gaske. Kamar dai yadda ku ka sani yan jarida da jami’an tsaron sun kasance tamkar dan jumma ne da dan jummai ;abun da ma ya kara kayatar da wasar ta yi armashi irin na gaske. > suite


Sarkin Damagaram ya sanya wani dan jarida zaman kaso a gidan tururuwa

Sarkin Damagaram (Zinder) ya sanya wani dan jarida zaman kaso a gidan tururuwa
jeudi 22 décembre 2005
A na maganin bakin abu dumya na hittowa. Gabe da lokacin da ministan maaikatar sadarwa ke cema gungun kungiyoyin yan jarida, tura keyar yan jarida a gidan wakafi ya kusa zama tarihi a kasar Nijar ko ma ya zama, albishir na cewa za a kadamar da kundin nan mai kumshe da ayoyin dokar da ke kare (...) > suite

Accueil du site | Contact | Plan du site | Espace privé | Statistiques | visites : 45639

Suivre la vie du site ha    ?

Site réalisé avec SPIP 1.9.2c + ALTERNATIVES

Creative Commons License